An kama waɗanda ake zargi da auren jinsi a Kano

An kama wasu mutane biyu da ake zargi da neman yin auren jinsi a Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, kwamandan Hisba ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar Asabar.

Ya kara da cewa an ga wasu samari guda biyu masu suna Khalifa da Abubakar a bidiyo suna kokarin sumbatar juna a wajen wani biki, wanda wata kila bikin aurensu ne.

Sai dai wadanda ake zargin sun musanta zargin cewa bikin ranar haihuwa ne maimakon bikin aure, kamar yadda aka yi ikirari.

Daya daga cikin wadanda ake zargin, mai suna Khalifa, ya bayyana cewa shi ne ya shirya bikin zagayowar ranar haihuwarsa, kuma abokinsa Abubakar ya kawo masa biredi.

Mutanen biyu suna hannun hukumar Hisbah, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...