An kama matashin da ya ƙone wata har lahira saboda zargin maita a Bauchi

Wani matashi dan shekara 30 mai suna Hamza Umar, ya shiga hannun jami’an ‘yan sanda a jihar Bauchi bayan da ya zuba wa wata yarinya kananzir da kone ta bisa zargin maita.

Wannan lamari dai an bayyana shi ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi, SP Ahmed Wakil, ya fitar.

Rundunar ‘yan sandan ta ce wanda ake zargin ya aikata laifin ne a lokacin da wanda ake zargin ta shiga gidansa da ke unguwar Rafin Albasa a cikin garin Bauchi babban birnin jihar, tana mai cewa babbar yayarta ce ta aiko ta domin ta kashe Hamzan.

“Wanda ake zargin ya ce ya yi yunkurin sa yarinyar ta bar gidansa, amma ya ce ta dage sai ta binne wasu laya a kusurwar gidan,” a cewar SP Wakili.

More News

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...