Rundunar ‘yan sandan jihar Borno a ranar Asabar ta yi nasarar ruguje shirin satar wasu taragogin jirgin kasa a tashar jirgin kasa da ke Maiduguri.
Wata majiya ta ce jami’an mutanen da ke yankin ne suka ba da rahoto wanda ya kai ha kama wadanda ake zargin.
Da aka tuntubi kakakin hukumar kula da jiragen kasa ta Najeriya Mahmood Yakubu, ya musanta labarin faruwar lamarin amma ya bukaci wakilinmu da ya tuntubi manajan yankin domin jin karin bayani.