An kai harin ‘ta’addacin majalisar dokokin Birtaniya

[ad_1]

Na’urarku na da matsalar sauraren sauti

An hango lokacin da Motar ta daki shinge binciken ‘yan sanda da gudu

Ana cafke wani mutum da ake zargi da ta’addanci bayan ya bi ta kan mutane da mota a wajen ginin majalisar dokokin Birtaniya.

Motar ta bi ta kan mutanen da ke tafiya a gefen hanya da misalin karfe 7:30 na safiya, inda ya jikkata mutum 3.

Babu wasu bayanai da ke nuna cewa mutum mai shekara 20 yana cikin mutane da hukumar leken asiri ta Birtaniya MI5 ko ‘yan sanda da ke yaki da’addanci ke sa ido a kansa.

Akwai wata mace guda cikin mutanen da suka jikkata da ake bai wa kulawar gaggawa sai dai raunin da ta samu ba wanda yake barazana ga rayuwarta ba ne.

Shugaban ‘yan sandan da ke yaki da ta’addanci a London, Neil Basu ya ce babu wata sauran barazanar tsaro da ake fuskanta a yanzu a birnin Landan, dama Birtaniya baki daya.

Image caption

‘Yadda ‘yan sanda suka tusa keyar mutum da ake zargi da kai harin.

Shaidu da dama sun ce da gangan matukin motar kirar Ford ya saki hannusa tare da buge mutane da ke kan kekuna da masu tafiya a kafa.

Hotunan BBC sun nuna lokacin da direban ya haye inda masu tafiya da kafa ke bi, kafin daga bisani ya tunkuyi shingayen binciken jami’an tsaro. An kuma hango lokacin da wani jami’in dan sanda ya arce daga kan hanya, gudun kar ya bi ta kan sa.

Yau dai ba a bude Majalisar ba. Kuma an rufe hanyar jirgin karkashin kasa a Westminister da wasu manyan tittuna da ke kewayen birnin.

Hotunan da aka wallafa a shafukan sada zumunta sun nuna yadda aka cafke wanda ake zargi tare da sa masa ankwa bayan faruwar al’amarin.

Image caption

Yadda Motar ta daki shinge binciken ‘yan sanda a Westminister

Wakiliyar BBC kan harkokin da suka shafi cikin gida June Kelly ta bayyana kamen a matsayin babban ci gaba.

”Yan sanda za su binciki mutumin da kuma asalinsa, watakila su gano haka ko suna kan hanyar gano hakan,” a cewar Kelly. ”Za su binciki abinda ya yi imani da shi, da mutanen da ya ke alaka da su, da lafiyar kwakwalwarsa.

Firaminista Theresa May ta ce: ”Hankalina na tare da wadanda suka jikkata a harin Westminister, kuma ina godewa sashin kai daukin gaggawa da bai yi kasa a gwiwa ba.”

Magajin garin London Sadiq Khan ya yi alla-wadai da faruwar lamarin da ya bayyana da halayen ‘yan ta’adda.


‘Shaidu na bayyana yadda suka tsere da ran su’

Barry Williams, wani ma’aikacin BBC da ke zaune a Millbank, ya ce: “na ji ihun ya yi yawa shi ne na juya.

“Motar ta saki hanya, ta koma hannun da ba nata ba, inda masu keke ke jiran a basu hannu, ta bi ta kan su.

“Direbar ya sake komawa kan titi ya karawa motar wuta da gudu ya tunkuyi shinge da ke kan hanya’

“Yar karamar motar ce ruwan azurfa, amma tsabar gudun da ya ke yi sai da motar ta yi sama sannan ta dawo kasa.


Hakkin mallakar hoto
Reuters

Image caption

An dakatar da hada-hadar motoci a Millbank

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Jami’an tsaro na ci gaba da shawagi a inda aka samu hatsarin

Sama da motar ‘yansanda 10 da motar bada agajin gaggawa akalla 3 aka girke a wajen ginin Majalisa bayan faruwar lamarin.

Jami’ai dauke da makamai da karnuka na cigaba da bincike a yankin.

‘Yan sandan Birtaniya da ke kula da sufuri sun ce za su karfafa matakan tsaro a Ingila da Scotland da Wales, kuma jami’ansu za su kasance cikin shirin ko-ta-kwana a tashohin jirage da Motoci

Image caption

Taswirar kewayen da lamarin ya faru a birnin Landan

[ad_2]

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...