Jami’an tsaro a ƙasar Iraƙi sun ce an kai hari da jiragen sama marasa matuƙa kan wani sansanin sojin Amurka da ke kusa da filin jirgin sama na Bagadaza, babban birnin ƙasar.
Rahotanni sun bayyana cewa gobara ta tashi sosai a cikin sansanin bayan harin. Sai dai har yanzu babu cikakken bayani kan ko harin ya jikkata ko ya halaka wasu mutane.
Harin ya faru ne ƴan sa’o’i kaɗan bayan da ofishin jakadancin Amurka da ke Bagadaza ya buƙaci dukkanin Amurkawan da har yanzu suke cikin Iraƙi da su fice daga ƙasar nan take.
A ranar Juma’ar da ta gabata ma an kai wani hari da jiragen sama marasa matuƙa kan ofishin jakadancin Amurka da ke Bagadazan.
Ofishin jakadancin ya ce ƙungiyoyin ƴan bindiga masu goyon bayan Iran suna kai hare-hare kan wuraren da ke da alaƙa da Amurka a Iraƙi, inda suke amfani da makaman roka da kuma jiragen sama marasa matuƙa.
An Kai Harin Jiragen Sama Marasa Matuƙa Kan Sansanin Sojin Amurka A Bagadaza

