An hana masu zanga-zanga fitowa a Kamaru

Paul Biya

— BBC Hausa

Image caption

Run a shekarar 1982 shugaba Paul Biya mai shekaru 85 ya ke mulkin Kamaru

Babbar jam’iyyar adawa a jamhuriyar Kamaru ta ce jami’an tsaro sun hana masu bore yin zanga-zanga a birnin Yaounde a ranar Asabar.

Jam’iyyar MRC dai ta shirya zanga-zangar matsawa gwamnati lamba ta saki jagoranta Maurice Kamto da ake tsare da shi.

A watan Fabrairu ne aka gurfanar da shi gaban kotun sojin kasar kan zargin kitsa bore da yi wa gwamnati zagon kasa, kuma daga lokacin aka tsare shi tare da wasu gwamman magoya bayansa.

An dai tsaurara matakan tsaron ne domin dakile zanga-zangar inda jami’an tsaro suka shirya tsaf domin watsawa masu zanga-zangar ruwan zafi.

To sai dai kuma magoya bayan jam’iyyar ta MRC sun sha alawashin cewa ba gudu ba ja da baya sai sun yi abinda suka yi niyya duk da jami’an tsaron da aka girke.

Kamen na zuwa ne bayan jam’iyyar MRC ta yi ta bore bayan zaben shugaban kasa a watan oktobar bara wanda ‘yan adawar suka ce an tafka magudi da aringizon kuri’u.

Lamarin da ya bai wa shugaba Poul Biya da ya dade kan karagar mulkin samun karin wani wa’adin, ya yin da Mr Kamto ya zama na biyu da yawan kuri’u.

More from this stream

Recomended