[ad_1]
An dakatar da sauka da tashin jirage a filin jirgin sama tilo da ke aiki a Tripoli babban birnin Libya.
Wani mai magana da yawun kamfanin jiragen sama mallakin kasar ya ce an dauki matakin ne saboda sun fahimci cewa a na kokarin kai wa filin jirgin saman hari da roka.
A na ci gaba da fada mai tsanani a unguwannin wajen Tripoli a wannan makon, inda a ka kashe kusan mutum arba’in.
A yanzu dai jirage na sauka da tashi a wani filin jirgi da ke birnin Misrata.
[ad_2]