An gwabza ‘kazamin fada’ tsakanin sojoji da Boko Haram a Borno

sojin Najeriya

Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta sun gwabza kazamin fada da mayakan Boko Haram a ranar Laraba, lokacin da ‘yan ta-da-kayar-bayan suka yi yunkurin kutsa wa garin Gashigar a jihar Borno da ke arewa maso gabashin kasar.

Mai magana da yawun rundunar Janar Texas Chukwu ya ce ‘yan ta-da-kayar-bayan sun je ne cikin manyan motoci guda tara, ‘ko da yake sun gamu da gamonsu a hannun dakarun kasar, inda suka yi musu fata-fata tare da haifar musu da asara ta mutane da kayan aiki.’

Sanarwar da rundunar ta fitar ta ce a yanzu haka dakarun sojin kasar sun mamaye yankin Gashigar da kewaye inda suke yin sunturi bayan faruwar lamarin.
Ta kuma bukaci da al’ummar yankin su kwantar da hankali tare da tabbatar musu da cewa suna cikin tsaro.A lokaci guda ita ma kungiyar IS a Afirka Ta Yamma ISWA, ta yi ikirarin kashe sojojin Najeriya bakwai tare da jikkata wasu a wani harin kwanton bauna ranar Larabar a garin Abadam.


Boko Haram a takaice

  • An kafa ta a shekarar 2002
  • Sunanta da Larabci shi ne, Jama’atu Ahlis Sunna Lidda’awati wal-Jihad
  • Ta fara aikinta ne da nuna kin jinin karatun boko
  • Ta kaddamar da kai hare-hare a shekarar 2009 da zummar samar da daular musulunci
  • Amurka ta ayyana ta a matsayin kungiyar ta’adda a 2013
  • Kungiyar ta ayyana wasu yankuna da ta kame a matsayin daulolin musulunci a shekarar 2014
  • A yanzu haka sojoji sun kwato mafi yawan yankunan
  • An samu rabuwar kai a shugabancin kungiyar tsakanin bangaren Shekau da na Al-Barnawi.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...