An gudanar da zanga-zangar adawa da rushe gine-gine a Kano

Daruruwan masu zanga-zanga sun bazama kan titunan jihar Kano inda suke nuna adawa kan rushe gine-gine da gwamnatin jihar ta ke yi.

Gwamnatin jihar Kano ta rushe gine-gine da dama a yayin da aka yi wa wasu alamar za a rushe su a nan gaba.

A cewar gwamnatin an dauki matakin ne saboda gwamnatin da ta gabata ta bayar da filayen gine-ginen ba bisa ka’ida ba.

Masu zanga-zangar na dauke da kwalayen da aka rubuta “Gwamna Yusuf abin da kake na korar masu zuba jari,” da sauran kalamai iri-iri.

Masu zanga-zanga sun taru ne otal din Daula da aka rushe inda suka wuce zuwa hedikwatar hukumar yan sanda ta jihar Kano domin su mika kokensu a hukumance.

More News

An kama mutane biyu  masu garkuwa da mutane a jihar Kogi

Wasu É“atagari biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne jami'an Æ´an sanda da haÉ—in gwiwar Æ´an bijilante suka kama a garin Ibobo-Abocho...

Jirgi mai saukar ungulu ya yi hatsari a Akwa Ibom

Wasu ma'aikatan kamfanin haƙar man fetur su 6 da kuma matuƙan jirgi su biyu su mutu a wani hatsarin jirgi mai saukar ungulu a...

Tinibu ya aikawa da majalisar dattawa sunaye 7 na  ministocin da zai naÉ—a

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga majalisar dattawa da ta tabbatar da sunayen mutane 7 da ya tura majalisar da zai...

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...