An garzaya da Abdulrashid Maina asibiti wanda ya sace kudaden yan fansho

Emmanuel Nweke mai taimakawa Abdulrashid Maina kan harkokin yada labarai ya ce maigidansa ya zame ya fadi a bakin ofishinsa dake Abuja a ranar Talata.

A wata sanarwa da ya fitar Nweke ya ce Maina ya zame lokacin da ya ke shiga ginin ofishinsa har ta kai kansa ya bugu da kafar bene abun da ya sa ya suma nan take.

Mataimakin na Maina ya alakanta faduwar da tayi kan matsanancin ciwon gwiwa da ya dade yana damun tsohon shugaban kwamitin shugaban ƙasa kan gyaran harkokin fansho.

” Jami’an kiwon lafiya dake wurin sun gaggauta bashi taimakon gaggawa kafin daga bisani a garzaya da shi wani asibiti mai zaman kansa Abuja domin samun kulawar likitoci,”

Sanarwar ta ce yanzu haka yana cigaba da samun kulawar likitoci kuma ɗaya daga cikin likitocin ya bada shawarar tanadar jirgin ɗaukar marasa lafiya domin kai shi kasar wajen matuƙar halin da ya ke ciki bai sauya ba zuwa wani dan lokaci.

Yan kwanakin da suka wuce ne aka sako Maina daga gidan yari bayan da ya kammala zaman hukuncin da aka yanke masa kan almundahanar kudaden fanshi

More from this stream

Recomended