An dakatar da sarkin da ya naɗa dan ta’adda Sarauta a Zamfara

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle ya dakatar da Sarkin Birnin Yandoto a karamar hukumar Tsafe ta jihar,Alhaji Aliyu Marafa bayan da ya naɗa wani kasurgumin dan bindiga, Ado Aleiro sarauta.

An naɗa Aleiro sarautar Sarkin Fulani a ranar Asabar.

A cewar sarkin an naɗa, Aleiro sarautar ne sakamakon rawar da ya taka wajen sulhun zaman lafiya tsakanin masarautar da kuma yan bindigar da suke addabar karamar hukumar Tsafe.

Amma kuma a wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar, Kabiru Balarabe Sardauna ya fitar gwamnatin ta nesanta kanta daga nadin sarautar da aka yi inda ta sanar da dakatarwar da gaggawa.

Tuni dai aka naɗa hakimin Yandoto, Alhaji Mahe Marafa domin ya cigaba da jagorantar masarautar.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...