An Dage Zaman Majalisun Tarayyar Nigeria

[ad_1]

Mai magana da yawun majalisar wakilai Abdulrazak Namdas a wata hira ta musamman da ya yi da wani gidan talibijan mai zaman kansa dake Abuja.

Ya ce a da sun amince dawowa aiki Talata amma babu alamun hakan zai yiwu. Yace sai shugabannin majalisun sun zauna a nan gaba su tsayar da ranar komawa aiki.

A bangaren majalisar dattawa Sanata Abu Ibrahim yace bas hi da masaniyar bude Majalisar. Saboda duk kafofin da ake bi na sanar da su ko rubuce, ko ta text, shi bai gani ba.

Batun canza shugabancin majalisun, musamman majalisar dattawa shi ne mutane ke harsashe a kai wanda shugaban RAPC Buba Galadima ya yi tsokaci akai.

Yace ba zancen kudin da za’a baiwa INEC ne dalilin son a bude majalisar saboda wai INEC na da kudi da za ta yi anfani dashi har zuwa watan goma na aikace aikacen ta. Ya ce me ya sa tuntuni ba’a kudin INEC cikin kasafin kudi, sai yanzu da ake son a labe da INEC din a tsige shugaban majalisa? Yana cewa abun kunya ne kuma ba zai yiwu ba bisa doka.

A nashi nazarin Farfesa Jibrin Ibrahim na cibiyar habaka Dimokradiya ya ce abun da doka ta tanada shi ne ‘yan majalisa zasu taru su zabi wanda suke so ya jagorancesu. A yawancin lokacin idan suna zabe zasu zabi wani daga bangaren dake da rinjaye ne. Injishi, a cikin wannan halin na baraka da canza sheka ba’a san wanda yake da rinjaye ba.

Sai dai wai dawowar nada nasaba ne da bukatar da shugaban kasa ke da ita na neman ‘yan majalisar su sa hannu a wasu bukatu.

A saurari rahoton Medina Dauda

[ad_2]

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...