
An binne gawarwakin mutane 10 mazauna ƙauyen Babuje dake karamar hukumar Barikin Ladi ta jihar Filato waɗanda aka kashe a wata mashaya a ranar Lahadi.
Wasu yan bindiga ne suka yi dirar mikiya a mashayar inda suka budewa mutanen dake zaune wuta.
Harin ya tilastawa mazauna garin rufe babbar hanyar Shendam zuwa Jos inda suka buƙaci kama waɗanda suka aikata laifin da kuma kawo ƙarshen abun da suka bayyana da mummunan aiki.
Wakilin jaridar Daily Trust ya rawaito cewa bikin binne mamatan ya samu halartar mutane da dama masu jimami da suka haɗa da iyalan mamatan, shugabannin al’umma da kuma shugabannin addini.
An gudanar da addu’oi na neman jinkai ga mamatan.
Gwamnatin jihar Filato ta fitar da wata sanarwa ranar Talata ta bakin Mrs Joyce Ramnap kwamishiniyar yada labarai da sadarwa inda ta ce gwamnatin jihar za ta tabbatar da cewa an kamo waɗanda suka aikata wannan mummunan laifin.

