Wata kotun majistare a Bauchi ya bayar da belin wa Dr. Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi.
Hakan na zuwa ne bayan an tsare shi na wasu sa’o’i a gidan yari.
Lauyoyin Dr. Dutsen Tanshi dai sun faÉ—a cewa wanda suke ba wa kariya ya cancanci a ba shi beli saboda hakan bai saba wa dokar Najeriya ba.
Idan ba a manta ba, wata kungiya da ake kira Fityatul Muslim ita ta kai shunensa ga hukuma da zargin cewa ya faÉ—i munanan kalamai ga Manzon Allah (SAW), wanda shi kuwa a nasa bangaren ya musanta hakan.