An ƙona sakatariyar ƙananan hukumomi 2 a jihar Rivers

Wasu da ake kyautata zaton ɓatagari ne sun ƙona wani sashe na sakatariyar ƙananan hukumomin Eleme da Ikwerre dake jihar Rivers.

Ƙona ginin na zuwa ƙasa da sa’o’i 24 bayan da Babban Sifetan Ƴan sandan Najeriya, Kayode Egbetokun ya bayar da umarnin janye ƴan sandan dake gadin ginin sakatariyar ƙananan hukumomin.

Grace Iringe-Koko mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Rivers ce ta bayar da sanarwar janye jami’an ƴan sandan.

Wasu daga cikin zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomin da kansilolinsu  da aka zaba ranar Asabar sun isa harabar sakatariyar inda suka iske ɓakin hayaki na tashi a inda yakamata ace ofishinsu ne.

Akwai rahotanni dake cewa wasu daga cikin ƴan siyasar jihar dake adawa da gwamna,Siminlayi Fubara na da hannu a ƙoƙarin tayar da tarzoma a jihar.

A ranar Asabar ne aka gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a jihar ta Rivers inda jam’iyar APP da gwamnan jihar ke marawa baya ta lashe kujerun ƙananan hukumomin jihar guda 23.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...