An ƙaddamar da matatar man Dangote

A yau Litinin ne matatar mai ta Dangote ta fara aiki.

An kera matatar man ne don fitar da ganga 650,000 a kowacce rana domin sarrafa ma’aunin danyen mai daga nahiyoyi uku na Afirka, Asiya da Amurka.

An kuma tattaro cewa matatar ta za ta kai rarar lita miliyan 38 na man fetur, dizal, kananzir da kuma man jiragen sama a kowace rana ga Najeriya.

Don haka za ta cika kaso 100 na man da kasar ke bukata.

Bayanai sun nuna cewa matatar ta Dangote za ta iya tallafawa wajen kafa gidajen mai guda 26,716, da samar da ayyukan yi na kai tsaye 100,000, da kuma samar da kasuwar danyen mai ta Najeriya $21bn a duk shekara.

More News

An Jikkata Jami’an Tsaro A Harin Da Ƴan Bindiga Su ka Kai Wa Ayarin Motocin Yahaya Bello

A jikkata wasu jami'an tsaro a wani hari da yan bindiga su ka kai kan jerin ayarin motocin gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ranar...

Bala Muhammad ya zama shugaban gwamnonin jam’iyyar PDP

An zaɓi gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad a matsayin sabon shugaban kungiyar gwamnonin jam'iyyar PDP. Siminalayi Fabura zaɓaɓɓen gwamnan jihar Rivers shi ne mataimakin shugaban...

Za mu sake bitar mafi karancin albashi a Najeriya—Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya yi alkawarin sake nazarin mafi karancin albashin ma’aikata domin dacewa da yanayin tattalin arzikin kasar nan. A cewarsa, akwai bukatar...

EFCC na zargin tsohuwar ministar mata a mulkin Buhari da karkatar da naira biliyan 2

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati ta titsiye tsohuwar ministar harkokin mata Pauline Tallen kan zargin azurta kai ta...