Ambaliya ta yi ɓarna a Gombe

Akalla gidaje 100 ne suka lalace sannan mutane 500 sun rasa matsuguni bayan ruwan sama na ranar Juma’a a jihar Gombe.

Lamarin wanda ya faru a unguwar Dogon Ruwa da ke karamar hukumar Kaltungo, ya kuma tafi da awaki 15.

Shugaban gargajiyar yankin, Aliyu Isah, ya bayyana cewa daga cikin dabbobin guda 15 akwai tumaki da awaki, inda ya kara da cewa ambaliyar ta yi mummunar barna ga mutanen.

Isah, wanda shi ne Sa’in Dogon Ruwa, ya shaida wa ƴan jarida cewa, mahukuntan karamar hukumar sun sani kuma har yanzu ba su dauki mataki ba.

Ya yi kira ga gwamnatin jihar Gombe da ta taimaka musu.

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...