Al’ummomin Wudil Sun Zargi ’Yan Sanda Da Kona Gidaje Kan Rikicin Filaye

Wasu al’ummomi a yankin ƙaramar hukumar Wudil a Jihar Kano sun zargi ’yan sanda da ƙone musu gidaje, wuraren sana’a, kayan abinci da kuma dabbobi, sakamakon wata hatsaniya da ta shafi mallakar gonaki.

Rikicin, wanda ke gaban kotu a halin yanzu, ya shafi mallakar gonakin wata fadama da ke tsakanin yankunan Wudil da Bunkure.

Mazauna ƙauyukan sun ce sun shafe ɗaruruwan shekaru suna zaune tare cikin zaman lafiya, inda auratayya da hulɗar kasuwanci ke haɗa su, kasancewar suna zaune a kan iyakar ƙananan hukumomin biyu.

Sai dai rikicin filayen noma, wanda ya fara sama da shekaru 20 da suka gabata, na barazana ga wannan kyakkyawar dangantaka da ta daɗe tana wanzuwa.

More from this stream

Recomended