Akwai ‘maciya’amana’ cikin ma’aikatan EFCC —Magu

[ad_1]

Ibrahim Magu

Hakkin mallakar hoto
Facebook/EFCC

Image caption

Ibrahim Magu ya ce za a hukunta maciya amana a cikin jami’an hukumar idan aka kama su

Shugaban hukumar EFCC mai yaki da masu yi wa tattalin arzikin Najeriya zagon kasa, Ibrahim Magu, ya ce akwai wadanda ake zargin maciya amana ne cikin ma’aikatan hukumar wadanda ke fallasa ayyukan hukumar ga ‘yan siyasa.

Magu, wanda ya fadi hakan a wajen wani taro na masu ruwa da tsaki a harkar yaki da cin hanci da rashawa, ya ce, hukumar tana bincike game da ire-iren wadannan jami’an.

Ya kara da cewa da zarar an gano irin wadannan jami’an a hukumar, za a hukunta su.

Magu ya ce irin nasarorin da hukumar ta samu a kotu kan tsofaffin gwamnoni biyu ya nuna cewa hukumar tana taka rawar gani wajen yaki da cin hanci da rashawa.

Shugaban hukumar ya ce irin wadannan nasarorin za su zama izina ga duk mai son halatta kudin haram a kasar.

Sai dai kuma tun ba yau ba wasu daga cikin ‘yan siyasa dake jam’iyyar hamayya ke ikirarin cewar EFCC tana nuna son kai wajen yakin da take yi da cin hanci da rashawa.

Kuma suna ikirarin cewar ba ta kama ‘yan jam’iyyar APC mai mulki.

Da aka yi masa tambaya game da wannan, sai shugaban hukumar ya ce babu ruwan EFCC da siyasa, kuma zargin ba zai hana hukumar yaki da cin hanci da rashawa ba.

[ad_2]

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...