Mai ɗakin tsohon shugaban Najeriya, Marigayin Muhammadu Buhari, Aisha Buhari, tare da ƴarta Hanan Buhari da wasu ƴan’uwanta, sun ziyarci jagoran adawar Najeriya, Atiku Abubakar, a masaukinsa da ke ƙasar Saudiyya.
Cikin wani saƙo da Atiku ya wallafa a shafukansa na sada zumunta, ya bayyana cewa: “Kamar dai ni, mai ɗakin tsohon shugaban ƙasar, da iyalanta na ƙasar Saudiyya domin gudanar da ibadar Umara.”
An bayyana cewa tun bayan rasuwar mijinta a watan Yuli 2025, Aisha Buhari ta fara ziyara a garin Daura da ke jihar Katsina, kafin daga baya ta koma Kaduna, inda ta kammala ibadarta.
Aisha Buhari Ta Ziyarci Atiku a Saudiyya Bayan Mutuwar Tsohon Shugaba Muhammadu Buhari

