Ahmed Nuhu Bamalli: Tarihin sabon Sarkin Zazzau | BBC Hausa

Ahmad Nuhu Bamalli

Bayan jan Æ™afa ta tsawon mako biyu da gwamnatin jihar Kaduna ta yi wajen naÉ—a sabon Sarkin Zazzau sakamakon mutuwar Sarki Shehu Idris, a Æ™arshe Gwamna Nasiru el-rufa’i ya sanar da naÉ—a Ahmed Nuhu Bamalli.

Bari mu yi nazari kan waye wannan sabon sarki da Masarautar Zazzau ta samu wanda shi ne na 19 a jerin sarakunan masarautar.

Ahmad Nuhu Bamalli ya fito ne daga gidan Mallawa, kuma shi ne Magajin Garin Zazzau kafin naÉ—insa sarki a ranar Laraba.

Ambasada Ahmed É—a ne ga Nuhu Bamalli tsohon Magajin Garin Zazzau kuma tsohon minista a Najeriya.

Magajin garin Zazzau wanda masani shari’a ne da diflomasiyya shi ne jakadan Najeriya a Thailand a yanzu.

Saboda girman sarautarsa ta Magajin Garin Zazzau da kuma kusancinsa da gwamnati shi ya sa aka dinga sanya shi a jerin waÉ—anda ka iya zama sabon Sarkin Zazzau na 19.

An haifi Ahmad Nuhu Bamalli a birnin Zaria ranar 8 ga watan Yuni na 1966.

Mahaifinsa, Nuhu Bamalli, yana cikin mutanen da suka yi fafutukar samun ‘yancin kan Najeriya kuma ya taba zama ministan harkokin wajen kasar sannan ya rike sarautar Magajin Garin Zazzau, wadda Alhaji Ahmed ya gada bayan rasuwarsa a 2001.

Sabon sarkin na Zazzau ya yi karatun firamare da sakandare a garin Kaduna, sannan ya tafi Jami’ar Ahmadu Bello, Zaria inda ya yi Digirinsa na farko a fannin lauya a 1989.

Kazalika ya yi Digirin Master’s a fannin harkokin kasashen duniya da diflomasiyya a Jami’ar ta Ahmadu Bello a 2002.

Jami’o’in da ya halarta domin yin wasu kwasa-kwasai sun haÉ—a da Harvard da Oxford da Northwestern University da ke Chicago da kuma Jami’ar Pennsylvania da ke Amurka.

Ahmed Nuhu Bamalli ya yi kusan ɗaukacin rayuwarsa ta aiki ne yana aiki a bankuna inda ya taɓa yin aiki a kamfanin da ke buga kudɗn Najeriya, Nigerian Security Printing and Minting.

A shekarar 2017 ne shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya naÉ—a shi a matsayin jakadan kasar a Thailand.

Gabanin nan, ya taɓa riƙe muƙamin Kwamishinan Hukumar Zaɓe ta jihar Kaduna.

Sabon sarkin na Zazzau yana da mata É—a, Mairo A Bamalli da kuma ‘ya’ya biyar – namiji É—aya da mata huÉ—u.

More News

Ƴan bindiga sun Æ™one ginin hedkwatar Æ™aramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu Æ´anta’adda da ke da alaÆ™a da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa Æ´an’adda a Borno, wani kwamanda ya miÆ™a wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...