Ahmed Musa ya bai wa marada kunya a wasan Supers Eagles da Seychelles

Ahmed Musa

Tawagar kwallon kafa ta Super Eagles ta doke ta Seychelles da ci 3-0 a wasan neman shiga gasar cin kofin nahiyar Afirka fafatawar rukuni na biyar.

Eagles wadda ta ziyarci Seychelles ta fara cin kwallo ta hannun Ahmed Musa minti 15 da fara tamaula, sannan Chidozie Awaziem ya kara ta biyu tun kafin aje hutu.

Bayan da aka dawo ne Odion Igahalo ya ci na uku a bugun fenariti.

Daya wasan rukuni na biyar din tashi suka yi babu ci tsakanin Afirka ta Kudu da Libya.

Da wannan sakamakon Libya tana mataki na daya a kan teburi da maki hudu, sai Afirka ta Kudu ita ma da maki hudu, sannan Nigeria ta uku da maki uku sai Seychelles wadda bata da maki a matsayin ta karshe.

Super Eagles za ta karbi bakuncin Seychelles a ranar 22 ga watan Maris, 2019.

Za a buga gasar cin kofin nahiyar Afirka a shekarar 2019 a Kamaru.

More News

Ƴansanda sun kama muggan ƴan fashi da makami

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Elemoro reshen jihar Legas sun kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a fashi da makami a...

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riÆ™aƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 Æ™irar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...