Afghanistan Ta Soki Hare-Haren Amurka Da Isra’ila Kan Iran

Ministan harkokin ’yan gudun hijra na kasar Afghanistan, Mohammed Kabir, ya bayyana abin da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya a matsayin “abin takaici ne kwarai”, inda ya ce gwamnatinsu ta yi Allah-wadai da hare-haren da Amurka da Isra’ila ke kai wa Iran.

Ministan ya bayyana hakan ne yayin wani bikin Idin Sallah Karama da aka gayyaci jami’an diflomasiyya, ciki har da jakadan Iran. Ya jaddada cewa wajibi ne kasashen Musulmai su nuna damuwarsu kan halin da ake ciki, yana mai cewa rikicin na barazana ga zaman lafiyar Gabas ta Tsakiya da ma duniyar Musulunci.

Tun da farko, a ranar Talata, ministan harkokin wajen Afghanistan, Amir Khan Muttaqi, ya yi kira ga Iran da ta yaki kasashen Gabas ta Tsakiya da ke mara wa Amurka baya.

More from this stream

Recomended