[ad_1]
Wani sabon salo a siyasar Najeriya shi ne na yadda mata masu yawa suka fito neman a zabe su a mukaman siyasa daban-daban da za a yi takararsu a shekarar 2019.
Wannan batu abin faranta rai ne ga yawancin mata, saboda karancin mata a cikin masu rike da madafan iko batu ne da ya dami ‘yan Najeriya da dama.
Amma duka da cewa matan sun fito sosai domin nuna kwarewarsu da cancantarsu, amma ana ganin jam’iyyun siyasa da wasu mazan na kokarin dakile wannan yunkuri na mata ‘yan siyasa.
Da alama an fara samun sauyin ra’ayi game da shigar mata fagen siyasa, amma tambayar ita ce shin suna samun nasarori kuwa?
A wannan makon, muna duba dalilan da suka sa mata ke kokawa duk da cewa al’ummar kasa na mara musu baya.
Shin kana iya zabar mace idan ta tsaya takara?
[ad_2]