ADC Ta Saka Ranar Rantsar Da Sabbin Shugabanninta A Najeriya

Jam’iyyar ADC ta haɗakar ƴan hamayya a Najeriya ta ayyana ranar 12 ga watan Mayu mai kamawa domin rantsar da sabbin shugabanninta a faɗin ƙasar.

A cikin wata sanarwa da kakakin jam’iyyar tsagin David Mark, Bolaji Abdullahi, ya fitar, jam’iyyar ta taya murna ga mambobinta da suka gudanar da tarukan jihohi domin zaɓen shugabanni, inda ta ce an yi su cikin kwanciyar hankali.

Sanarwar ta ce, “Wannan ya nuna muradin jam’iyyar na yin abubuwanta cikin kwanciyar hankali da lumana tare da bin tsarin dimokraɗiyya da martaba doka”.

Haka kuma, jam’iyyar ta buƙaci sabbin shugabannin jihohi su yi aiki tare da uwar jam’iyya ƙarƙashin jagorancin David Mark domin ƙarfafa ADC a faɗin ƙasar.

Sai dai tun da farko, shugaban hukumar zaɓen ƙasar, Farfesa Joash Amupitan, ya gargaɗi jam’iyyar kada ta gudanar da irin waɗannan zaɓuka, yana mai cewa hakan ya saɓa da hukuncin kotu da ya rushe shugabancin jam’iyyar.

More from this stream

Recomended