Adamawa: An kama wadanda ake zargin sun kashe wasu mata saboda zargin maita

Wasu gungun mutane sun kashe wasu mata biyu a jihar Adamawa bisa zargin su da maita.

Rahotanni sun nuna cewa wani sufeton ‘yan sanda da kuma wasu ‘yan banga na da hannu a kisan.

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa, wacce a ranar Lahadin da ta gabata ta tabbatar da faruwar lamarin, ta ce ta kama wasu mutane 10 da ake zargi da hannu a ciki, ciki har da dan sanda da kuma ‘yan banga.

Rundunar, a cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na ƴan sandan jihar, SP Suleiman Nguroje ya sanya wa hannu, ta ce, “Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta ci karo da wani faifan bidiyo mara dadi wanda ya yadu a wasu sassan kafafen yada labarai, musamman a shafukan sada zumunta, inda wani Sufeto na ‘yan sanda da kuma wasu ‘yan banga da ke hedikwatar ‘yan sanda na Dumne, inda aka gan su suna cin zarafin mata uku ta hanyar da ba ta dace ba.

More News

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...

AMBALIYA: Bafarawa ya ba wa al’ummar Sokoto gudunmawar naira biliyan 1

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Bafarawa, ya bayar da gudummawar Naira biliyan daya ga al’ummar Sokoto, domin rage radadin wannan annoba.An bayyana hakan...

Ƴanbindiga sun kai hari coci-coci a Kaduna, sun kuma yi garkuwa da mutane

Mutane 3 ne ake fargabar sun mutu, sannan an yi garkuwa da wasu 30 bayan wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a...