Sama da naira biliyan 3 aka tara a wurin taron gidauniyar sake gina masallacin Juma’a na masarautar Zazzau.
Gudunmawa mafi tsoka ta fito ne daga hannun mai kaddamarwa kuma shugaban kamfanin BUA, Alhaji Abdulsamad Isyaka Rabiu wanda ya bayar da naira biliyan biyu.
Mataimakin mai kaddamarwa, Alhaji Dahiru Barau Mangal ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 shima Mista Wale Tinubu ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 a yayin da shima Alhaji Musa Bello ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100.
Alhaji Yahaya Bello, Alhaji Kassim Bukar, Alhaji Aliyu Dikko da Alhaji Sulaiman Barau kowannensu ya bayar da gudunmawar naira miliyan 50.
Taron gidauniyar samar da kudin sake gina masallaci ya gida ne a cibiyar taro ta Shehu Musa Yaradua dake Abuja da yammacin ranar Asabar.