Abba Ganduje ya rabawa matasa injin ban ruwa mai amfani da hasken rana

Hukumar samar da wutar lantarki a karkara REA ta raba injinan ban ruwan rani dake aiki da hasken rana ga manoma a jihar Kano.

Umar Abdullahi Ganduje daraktan fasaha a hukumar shi ne ya jagoranci rabon a wani taro da aka gudanar a ranar Lahadi.

Ganduje ya raba injin ban ruwan ranin mai amfani da hasken rana ga matasan manoma 120 da kuma na’urar bada wutar lantarki ta hasken rana ga masu matsakaita da Æ™ananan sana’o’i su 160 da suka fito daga Æ™ananan hukumomin Dawakin Tofa, Tofa da kuma Rimin Gado.

Jumullar mutane 280 ne suka amfana da shirin a ƙananan hukumomin uku.

A wata sanarwa da aka fitar ranar Litinin, Edwin Olofu mataimaki kan harkokin yada labarai ga Abdullahi Umar Ganduje tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa ya ce duka waÉ—anda suka amfana sun samu na’urar samar da lantarki da hasken rana mai karfin kilowat.

Olofu ya ce kayan da akan raba za su taimakawa mutanen da suka amfana a wajen sana’arsu tare ga masu dogaro da man fetur.

More from this stream

Recomended