Kungiyar kwadagon Najeriya ta dakatar da yajin aiki

Kungiyar kwadagon Najeriya ta dakatar da yajin aikin gama garin da take yi don menan karin albahi.

Shugaban kungiyar Ayuba Wabba ne ya sanar da dakatar da yajin aikin a wani taron manema labarai a Abuja ranar Lahadi.

Ya ce dakatar da yajin aikin ya fara aiki ne daga ranar Lahadin.

Sai dai kuma ma’aiakta da dama ba za su yi aiki ranar Litinin ba domin hutun bikin samun ‘yancin kan Najeriya.

Kungiyar kwadagon tana neman a kara wa ma’aikata albashi ne daga mafi karancin albashin naira 18,000 zuwa kimanin naira 50,000.

Shugaban kungiyar kwadagon ya bukaci gwamnatin kasar ta dawo da kwamitin tattaunawa.

Sannan ministan kwadagon Najeriya, Chris Ngige ya tabbatar da cewa gwamnati za ta dawo da kwamitin tattaunawa tare da yin la’akari da bukatun kungiyar a ganawar da za su yi nan gaba.

More News

Atiku ya bayar da tallafin miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri babban birnin...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

Mutanen Sokoto na ta murnar kashe ƙasurgumin ɗanbindigar nan Halilu Buzu

Mazauna yankin Sokoto da kewaye na murnar kashe wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Kachallah Halilu Buzu, da sojojin Najeriya suka yi a farmakin da...