Jonathan ya samu damar ficewa daga Guinea Bissau bayan juyin mulki

Gwamnatin tarayya ta ce tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan na nan kalau kuma ya fice daga ƙasar Guinea Bissau bayan da sojoji suka yi juyin mulki a kasar.

A wata sanarwa ranar Alhamis, Kimiebi Ebienfa mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, ya ce Jonathan ya bar kasar ta Guinea Bissau a wani jirgin na musamman tare da yan tawagarsa.

“Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya na nan kalau cikin lafiya kuma ya fice daga ƙasar Guinea Bissau. Ya bar kasar a cikin wani jirgi na musamman tare da yan tawagarsa ciki har da Muhammad ibn Chambas,” a cewar Ebienfa a cikin sanarwar da ya fitar.

Tsohon shugaban kasar yaje kasar ne domin sanya idanu a zaɓen shugaban kasar da aka gudanar.

A ranar Laraba ne sojoji suka sanar da karɓe Mulki a kasar dai-dai lokacin da ake dakon sakamakon zaɓen shugaban kasar da aka gudanar.

More from this stream

Recomended