
Omoyole Sowore dan gwagwarmaya kuma mai fafutukar kare hakkin bil’adama ya fito daga gidan yarin Kuje bayan da ya cika sharudan beli da kotu ta gindaya masa.
An sako Sowore a ranar Litinin tare da Aloy Ejimakor tsohon lauyan Nnamdi Kanu da kuma wasu mutane 11 da suka shiga zanga-zangar neman sakin Nnamdi daga hannun jami’an tsaro.
Tun shekarar 2021 ne Nnamdi Kanu ya ke tsare a hannun jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS tun bayan da suka kama shi.
A ranar Juma’a ne yan sanda suka gurfanar da wasu mutane 11 tare da Sowore da Ejimakor a gaban kotu inda ake tuhumarsu da tayar da hankalin jama’a bayan da suka shiga zanga-zangar da aka kira FreeNnamdiKanu wacce aka gudanar a birnin tarayya Abuja .
Alkalin Wata kotun majistire dake Abuja ne ya bayar da belin mutanen bisa sharadin cewa kowannensu zai kawo mutum biyu da za su tsaya masa kan kudi naira ₦500,000,
Har ila dole mutanen su gabatar da nambarsu ta NIN, shedar biyan haraji da kuma fasfonsu na tafiye-tafiye.

