EFCC Ta Cafke Ƴan China 4 Da Wasu 27 Kan Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba a Jihar Filato

Hukumar Yaki da Masu Yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta cafke wasu mutane 31, ciki har da Sinawa hudu, bisa zargin hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a Jos, babban birnin Jihar Filato.

Mai magana da yawun hukumar, Dele Oyewale, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata a Abuja.

A cewar sanarwar, an kama mutanen ne a ranar Asabar a harabar kamfanin Jiasheng Nigeria Limited da ke Dura Rayfield, kan titin Mangu a Jos.

Oyewale ya ce kama su ya biyo bayan samun sahihan bayanai da suka danganta kamfanin da ayyukan hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a jihar.

Ya bayyana cewa cikin mutanen da aka kama, akwai Sinawa hudu da kuma ‘yan Najeriya 27 da ke da hannu a harkar, ciki har da masu kawo ma’adanai da ba a tace ba, wadanda ake zargin an hako su ne ba bisa ka’ida ba.

Haka nan, hukumar ta ce ta samu wasu kayayyakin shaida a wurin, ciki har da wata motar daukar kaya cike da buhuna takwas na Monazite da aka tace, wanda kowanne buhu ke da nauyin kilogiram 1000. Ana kiyasta darajar kowanne buhu a kan naira miliyan hudu.

EFCC ta tabbatar da cewa za a gurfanar da wadanda ake zargi a kotu da zarar an kammala bincike.

More from this stream

Recomended