Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce adadin maniyyata 18,906 na shekarar 2024/1445 aka yi jigilarsu zuwa kasar Saudiyya.
Hukumar ta bayyana hakan ne a rana ta 11 ta jigilar.
Rahotanni sun ruwaito cewa an yi jigilar maniyyatan da aka ambata a cikin jirage 45.
Sai dai jihohi 23 a Najeriya ba su fara jigilar maniyyata aikin hajjin 2024 ba, inji rahotanni.
Maniyyayan Najeriya sama da 18,000 sun isa Saudiyya
![Nigerian-Hajj-pilgrims.jpg](https://arewa.ng/wp-content/uploads/Nigerian-Hajj-pilgrims.jpg)