Buhari ya ce ba zai fadi mutanen da zan nada ministoci ba

Shugaba Muhammadu Buhari ya ce ba zai ce komai ba game da kunshin mutanen da za su kasance a sabuwar gwamnatinsa.

Da yake amsa tambayoyi daga manema labarai bayan da ya dawo daga kasar Birtaniya. Buhari ya ce a shirye yake ya zauna ya rantsar da sabbin ministocinsa.

Wani dan jarida ya tambaye shi “wadanne irin mutane ne za su kasance a cikin gwamnatinka da za a kafa?.” inda ya kada baki yace: “bazan fada maka ba.”

Kan yawan kashe-kashe dake faruwa a sassan kasarnan.Buhari ya ce ya lura Muhammad Adamu mai rikon mukamin babban sifetan ƴansanda na kasa ya rame wannan wata alama ce dake nuna cewa yana aiki.

More from this stream

Recomended