2027: NNPP Ta Karyata Rahoton Shirin Kwankwaso Na Komawa APC


Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) ta musanta rahotannin da ke cewa tsohon ɗan takararta na shugaban ƙasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, na tattaunawa da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) domin komawa cikinta.

Sakataren ƙasa na jam’iyyar NNPP, Dipo Olayoku, ya bayyana cewa babu wani lokaci da Kwankwaso ya taɓa yin irin wannan tattaunawa da APC. Ya ce rahotannin da ke yawo ba su da tushe balle makama.

A wata hira da Trust TV, Olayoku ya ce ganawar ƙarshe da Kwankwaso ya yi da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta kasance ne a watan Janairun 2024, tare da Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf. A cewarsa, ziyarar ta biyo bayan hukuncin Kotun Ƙoli ne wanda ya tabbatar da nasarar NNPP a Kano.

Olayoku ya ƙara da cewa tun daga wannan lokaci, babu wata tattaunawa tsakanin Kwankwaso da APC. Ya kuma zargi wasu da yaɗa farfaganda, inda ya ce an taɓa yaɗa labarin cewa Kwankwaso na ganawa da Shugaban Ƙasa a Aso Rock, alhali a lokacin yana tare da su a gidansa.

Ya bayyana cewa irin waɗannan jita-jita an ƙirƙire su ne domin ruɗa jama’a, yana mai jaddada cewa Kwankwaso bai da niyyar barin NNPP.

More from this stream

Recomended