
Kwana guda bayan mutuwar mahaifiyarsa sai gashi gwamnan jihar Jigawa, Umar Namadi ya yi rashin ɗansa, Abdulwahab mai shekaru 24.
A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Hamisu Gumel ya fitar ya ce Abdulwahab ya rasa ransa ne a wani hatsarin mota a ranar Alhamis.
” A cikin alhini tare da miƙa kai ga ƙaddarar Allah, Mai Girma, Mallam Umar Namadi gwamnan jihar Jigawa na sanar da sake mutuwar wani daga cikin iyalansa; ɗansa Abdulwahab Umar Namadi, ” a cewar sanarwar.
Sanarwar ta kara da cewa marigayin ya rasu ne wani mummunan hatsarin mota da ya faru ranar Alhamis akan hanyar Dutse zuwa Kafin Hausa.
An yi jana’izar marigayin a garin Kafin Hausa.