Ƴantq’qdda Sun Kqshe Sojoji 9 Da Babban Limamin Wani Gari A Borno

Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram/ISWAP ne sun kashe aƙalla sojojin Najeriya tara tare da Babban Limamin wani gari bayan kai wani hari da suka yi a Ngoshe, ƙaramar hukuma ta Gwoza a jihar Borno.

Majiyoyin tsaro sun ce harin ya faru ne a daren ranar Talata, jim kaɗan bayan al’ummar yankin sun sha ruwan azumin watan Ramadan.

Wata majiya ta tsaro wadda ta nemi a sakaya sunanta ta ce maharan sun iso da yawa kuma dauke da manyan makamai. Ta ce sun kai hari kan sansanin sojoji da ke yankin, inda suka fi sojojin ƙarfin wuta.

Wata majiya ta daban ta ce maharan sun kuma shiga cikin garin Ngoshe, inda suka kashe Babban Limamin masallacin garin tare da sace sama da mata da yara 100. Ta ce wasu mutane ma sun jikkata a harin.

Majiyar ta ce: “Yanzu da nake magana da kai, duk mutanen Ngoshe sun tsere, babu wanda ya rage a cikin garin. Yawancinmu mun tsere zuwa Pulka domin neman mafaka.”

Ta kuma yi zargin cewa maharan sun samu taimako daga wani mutum daga cikin al’ummar garin.

Ta ce: “Sun zo cikin shiri kuma suka shiga garin Ngoshe da taimakon wani daga ciki, inda suka kashe sojoji 9, suka yanka Babban Limamin masallacin, sannan suka yi awon gaba da sama da mata da yara 100.”

More from this stream

Recomended