Ƴanbindiga sun kashe mutane a Filato

Wasu ‘yan bindiga sun halaka mutane biyar a kauyen Mbar da ke karamar hukumar Bokkos a jihar Filato.

Sanarwar da Barista Farmasum Fuddang, shugaba, da Amb.  Duwam Bosco, sakataren kungiyar Bokkos Cultural Development Council Vanguard (BCDCV), a Jos, ita ta bayyana hakan.

A cewarsu, “Muna so mu yi Allah wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasa biyar da ba su ji ba ba su gani ba a yankin Mbar a ranar 15 ga watan Satumba, duk da rahotannin sirri da aka samu a baya na kwararar ‘yan ta’adda a yankin.”

Sanarwar ta bayyana cewa, an far wa matasan, wadanda ba su da makami, a kan hanyarsu ta daga garin Mbar zuwa kauyen Koh a kan wata hanya da ta kewaya kauyen Yelwa Nono da misalin karfe 7 na dare zuwa karfe 7:30 na dare, inda ‘yan ta’addan suka tsere kan babura wadanda tun farko sojoji suka fatattake su daga kewayen wajen.

Jihar Filato dai takan fuskanci irin waɗannan hare-haren.

More News

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...

Mutane 18 sun ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota

Aƙalla fasinjoji 18 ne suka ƙone ƙurmus a wani hatsarin mota da ya faru akan babbar hanyar Ojebu-Ode zuwa Ore a yankin Ogbere dake...