Ƴan ta’adda sun ɗaura wa manoma haraji a Zamfara

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Tangaza/gudu ta jihar Sokoto a majalisar wakilai ta tarayya, Hon. Sani Yakubu ya ce ‘yan bindiga daga Nijar da Mali da Libya da takwarorinsu na kananan hukumomin Tangaza na jihar sun sanya haraji kan manoma.

Yakubu, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake gabatar da kudiri a zauren majalisar a ranar Larabar da ta gabata, ya ce mazabar Tangaza/Gudu na kewaye da dazuzzuka biyu; Dajin Tsauna wanda ya ratsa zuwa Gwadabawa, Illela da Jamhuriyar Nijar da dajin Kuyan Bana wanda ya kai Gudu da Jamhuriyar Nijar.

Dan majalisar ya ce ‘yan ta’addan da ke yin sintiri a wurin sun hada karfi da karfe, lamarin da ya sa jami’an tsaron da aka tura ke da wuya su magance matsalar rashin tsaro a yankin baki daya.

Yakubu ya kara da cewa, duba da yadda al’ummar yankin galibi manoma ne, ‘yan fashin sun sha alwashin dakatar da ayyukan noman na bana idan al’ummomin suka ki biyan harajin da aka dora musu.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...