Ƴan sanda sun kama mutane 4 da suka sace kayan tallafin ambaliyar ruwa a jihar Borno

Rundunar ƴan sandan jihar Borno ta ce ta kama mutane huɗu da aka samu da sace kayayyakin tallafi da aka bawa mutanen da ambaliyar ta shafa a jihar.

Mutanen da suka faɗa hannun rundunar sun haɗa da Abubakar Usman, mai shekaru 32, Mohammed Bukar,mai shekaru 37, Ibrahim Abubakar, mai shekaru 28, da kuma  Jamilu Mohammed, mai shekaru 24.

Ambaliyar ruwan da ta faru a ranar 10 ga watan Satumba ta raba dubban mutane da gidajensu musamman a yankunan Fori, Galtimari, Gwange, da kuma  Bulabulin dake  Maiduguri.

Bayan ambaliyar ruwan gwamnatin jihar Borno ta karɓi tallafi daga dai-dai kun mutane, hukumomi, kamfanoni, gwamnatocin jihohi da gwamnatin tarayya.

Da yake magana a wurin wani taron manema labarai ranar Alhamis,Daso Nahum mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Borno ya ce waɗanda ake zargin sun sace kayan tallafin daga wata cibiyar raba kayan dake makarantar  Firamaren Babagana Wakil Memorial dake Maiduguri.

A cewar Nahum kayan da aka sace sun hada da buhun shinkafa 5 mai nauyin 25kg, barguna guda shida,katan ɗin makaroni biyu, tabarmi shida sai kuma gidan sauro guda uku.

Ya ƙara da cewa waɗanda ake zargin sun amsa laifinsu kuma nan bada jimawa ba za a gurfanar da su a gaban kotu.

More News

TCN na ci gaba da ƙoƙarin gyaran wutar lantarkin da ta lalace kwana biyu

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya sanar da ci gaban da aka samu wajen farfado da rukunin wutar kasa bayan wata tangardar...

Magoya bayan jam’iyyar NNPP sun ƙona jar hula

Wasu daga cikin mambobin wani tsagi na jam'iyar NNPP sun barranta kansu da jagoran jam'iyar na ƙasa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso inda suka riƙa...

PDP ta ɗauki hanyar warware rikicin jam’iyyar

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya ce  an kawo karshen rikicin cikin gida da ya dabaibaye jami'yar PDP. Mohammed wanda shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin...

Dakarun Najeriya sun cafke wasu ƴan’aiken ƴanbindiga a Kaduna

Sojoji sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da kaiwa 'yan bindiga sakonninsu a kasuwar ƙauyen SCC da ke ƙaramar hukumar Kachia a...