Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara ta sanar da kama mutane 21 da ake zargi da yin hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, a wani samame da aka gudanar a kananan hukumomin Zurmi da Maradun na jihar.
Mai magana da yawun rundunar, DSP Yazid Abubakar, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi. Ya ce kamen ya biyo bayan wani farmaki na hadin gwiwa da jami’an Sashen Yaki da Hakar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba, Sashen Ayyuka na Musamman, da Sashen Kula da Bama-bamai suka kai a ranar Asabar.
A cewarsa, an gudanar da aikin ne tare da hadin kan jami’an Hukumar Tsaro da Kare Fararen Hula (NSCDC), da kuma jami’an Ma’aikatar Ma’adinai ta Tarayya, reshen Gusau.
DSP Abubakar ya ce an kai samamen ne a kauyen Boko da ke Zurmi da kuma kauyen Kaya a Maradun, bayan samun rahotannin ci gaba da ayyukan hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a yankunan.
Ƴan Sanda Sun Kama Mutane 21 Da Ake Zargi Da Hakar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba A Zamfara

