Ƴan Najeriya Suna Ta Martani Kan Sanya Sunan Kwankwaso Cikin Jerin Masu Take Hakkin Kiristoci Da Amurka Ta Yi

’Yan Najeriya na ci gaba da nuna rashin jin dadinsu bayan da wasu ’yan majalisar dokokin Amurka suka ayyana sunan jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, cikin jerin mutanen da ake zargi da take hakkin Kiristoci a Nijeriya.

Rahotanni sun ce wasu ’yan majalisar dokokin Amurka guda biyar ne suka sanya sunan tsohon gwamnan Jihar Kano a cikin jerin sunayen, a wani kudirin doka da suka gabatar a gaban zauren majalisar dokokin kasar ranar Talata.

Matakin ya jawo ce-ce-ku-ce a tsakanin ’yan Najeriya, inda da dama ke mayar da martani kan zargin da aka jingina masa, yayin da ake ci gaba da tattaunawa kan sahihancin batun da dalilan da suka haddasa daukar wannan mataki.

Mutane da dama sun zargi majalisar Amurkar da farfaganda.

More from this stream

Recomended