
Ƴan Najeriya na ci gaba da mayar da martani kan umarnin sake buɗe kan iyakokin tudu guda huɗu da shugaba Muhammadu Buhari ya bayar da yammacin jiya Laraba.
A cikin watan Agustan bara ne, gwamnatin ƙasar ta sanar da rufe kan iyakokin da nufin daƙile fasa-ƙwaurin shinkafa da makamai.
Gwamnatin dai ta sha cewa kwalliya ta biya kuɗin sabulu wajen rufe iyakokin.
Sake buɗe iyakokin a wannan lokaci yazo da bazata kuma babu wani dalilai da gwamnati ta bayar da suka sa aka sake buɗe su, duk da cewa ƴan ƙasar sun daɗe suna fatan ganin hakan.
Amma mai ba wa shugaba Buhari shawara kan harkokin yada labarai Garba Shehu, ya shaida wa BBC cewa an buɗe iyakokinne sakamakon shawarar da wani kwamiti na musamman da shugaban ƙasar ya kafa kan matsalar rufe iyakar.
Sai dai Dr Abdurrazak Ibrahim Fagge, shugaban sashen nazarin tattalin arziki a jami`ar Yusuf Maitama Sule a Kano ya shaida wa BBC cewa buɗe iyakokin, shi ne mafi alheri.
Rufe iyaka kuskure ne
Dr Abdurrazak, ya ce dama matakin da aka ɗauka tun da fari na rufe iyakokin Najeriya an yi su ne bisa kuskure saboda babu ƙasar da ake rufe iyaka a yanzu.
Akwai matakai daban-daban da ake ɗauka kamar haraji da lasisi da rage yawan abin da ake shigarwa ko fita da shi.
Rufe iyakokin sun janyo matsaloli da yawa kuma ita gwamnati ta fahimci hakan, saboda a baya-bayan nan alkaluman cibiyar tattalin arziki ya nuna matuƙar koma baya da Najeriya ta samu a fannin cinikayya.
Najeriya ta samu naƙasu a zango na 3 na shekara mai ƙarewa da sama da naira triliyan 2.
Yanzu an zo kuma gaɓar da gwmanati ke son soma shigo da man fetur daga Nijar don haka ya zame mata tilas shi yasa ta bude.
Kafin rufewar akwai ƙananan masana’antu da ke kai kayansu ƙasahe makwabta kamar Nijar da Chadi, wanda rufe iyakar ya durƙusar da su.
Sannan a yanzu akwai manoma da aka tilasta wa zuba kuɗi a harkar noma, mutane da yawa sun zuba kuɗaɗe wajen kafa masana’antun shinkafa don haka akwai yiwuwar su faɗa cikin matsala
Amma duk da haka bude iyakokin shi ne alheri saboda a tsari na tattalin arzikin duniya babu batun rufe iyaka.
Amma dole gwamnati ta agazawa manoma wajen nema musu sassauci domin saɓanin hakan zai jefa su cikin tasku.
Ya ƴan Najeriya suka ji?
Galibi dai farin ciki ne ta kowanne ɓangare musamman ga ƴan kasuwa da wannan hanya ce madogara a rayuwarsu.
Da dama daga cikin mutanen da BBC ta zanta da su na ganin lokaci ya yi da rayuwa zata dawo musu dai-dai bayan shafe tsawon lokaci ana wahala.
Masu koke da matsin rayuwa na ganin wannan nasara ce domin kasuwa zata buɗe da cire su daga matsin rayuwa.
Akwai ma masu ganin har a fannin tsaro ana iya samun sauƙi, abinci zai yi sauƙi.
Karin haske
A bara gwamnatin shugaba Buhari ta ce ta ɗauki matakin rufe iyakokin ƙasar ne da nufin daƙile ayyukan fasa-ƙwauri musamman na shinkafa.
Sannan gwamnatin cikin dalilan nata har da ƙoƙarinta na hana fasa ƙwaurin miyagun ƙwayoyi da makamai waɗanda suke barazana ga tsaro.
To amma wannan mataki ya ja hankalin mutane da dama a ƙasar tare da jawo ce-ce-ku-ce, inda wasu ke goyon baya wasu kuma ba sa goyon baya.
Shugabannin ƙasashe maƙwabtan Najeriya sun daɗe suna roƙon shugaba Buhari da ya buɗe iyakokin.
An shiga mawuyacin yanayi na tsadar abinci, kuma lamarin ya tilastawa galibin mutane koma wa noma su kuma manoma sun more ganin ƙasar ta dogara da abin da suke nomawa.
Sai dai kamar yadda masu sharhi ke cewa komai ba ya rasa alfanu da akasin haka, duk da cewa buɗe iyakar yafi alfanu akwai masu ganin hakan zai durƙusar da ƴan kasuwar da suka farfaɗo sanadiyar rufe iyakokin.
A yanzu dai dukkan iyakokin da aka bayar da izinin buɗewa waɗanda suke kan iyakar ƙasar ne da jamhuriyyar Nijar da ta Benin.