
Shugaban majalisar dokokin jihar Adamawa, Bathiya Wesley ya fice daga jam’iyar PDP tare da wasu mambobin majalisar su 13.
A yayin zaman majalisar na ranar Laraba akawun majalisar Umar Usman Hamid ya karanta yadda zaman majalisar na ranar zai kasance bayan nan ne kuma shugaban majalisar Bathiya Wesley ya sanar da sauran yan majalisar ficewarsa daga jam’iyar PDP.
Sauran waɗanda su ka fice daga jam’iyar ta PDP sun haɗa da mataimakin shugaban majalisar, Muhammad Buba Jidjiwa dake wakiltar mazabar (Jada-Mbulo), Kefas Calvin(Toungo), Bulus Geoffrey (Leko – Koma) da kuma Haruna Jilantikiri (Madagali).
Sauran sun hada da Kefas Emmanuel, (Song), Ahmed Jingi Belel (Maiha), Hon. Moses Yerima Zah (Michika), Hon. Kate Raymond Mamuno (Demsa), Pwamwakeno Mackondo (Numan), Adun John Alaba(Uba -Gaya), Bulus Kantom (Shelleng) , Hon. Musa Mahmud Kallamu (Mayo Belwa) da kuma Japhet Hammanjabu mamba mai wakiltar mazabar (Verre).
A yayin zaman majalisar ba aga keyar Hon.Bauna Myandiasa mamba mai wakiltar mazabar Lamurde.
Shugaban kwamitin yaɗa labarai na majalisar, Mahmud Kallamu ya ce waɗanda su ka sauya shekar su na tattaunawa da al’ummar da su ke zabe su domin fitar da matsaya kan jam’iyar da za su koma.
Kallamu ya ce za su bi duk wata alkibla da gwamnan jihar Ahmadu Fintiri ya zaba.

