Ƴan kwadago ba su fasa zanga-zanga ba duk da shirin Tinubu kan rarar tallafin mai

Kungiyar kwadago ta ce za ta gudanar da zanga-zangar da ta shirya yi a fadin kasar ranar Laraba duk da bayani game da shirin cire tallafin da shugaban kasa Bola Tinubu ya yi.

Tinubu ya bayyana hakan ne a wani jawabi inda ya ce an ware N500bn ga masana’antu, kananan ‘yan kasuwa da manoma. Ya kuma fitar da shirye-shiryen kara albashi da kuma sayen manyan motocin bas guda 3,000.

Duk da yunkurin da shugaban kasar ya yi na dakile zanga-zangar ƴa kwadagon, shugaban kungiyar ta Najeriya, Joe Ajaero, ya ce ba za su fasa zanga-zangar ba.

Ajaero ya yi magana ne jim kadan bayan tattaunawa tsakanin kungiyoyin kwadago da gwamnatin tarayya a ranar Litinin din da ta gabata, inda ba a cimma matsaya ba. Ana sa ran za a ci gaba da tattaunawa ranar Talata (yau).

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...