Ƴan fashin daji sun kashe ƴan bijilante 4 da ɗan sanda ɗaya a Kaduna

Wasu da ake zargin ƴan fashin daji ne sun kai farmaki mazaɓar Kakangi dake ƙaramar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna inda suka kashe ƴan bijilante huɗu da kuma ɗan sandan kwantar da tarzoma guda ɗaya

Ƴan bindigar sun kuma yi garkuwa da mutanen da basu san adadinsu ba a kusa da wata gona dake yankin Sabon Layi  duka a mazaɓar.

Yahaya Musa Dan Salio mamba mai wakiltar al’ummar mazaɓar Kutemeshi a majalisar dokokin jihar Kaduna ya tabbatarwa da jaridar Daily Trust faruwar lamarin a ranar Litinin.

Ya ce ” Eh a cikin waɗanda abin ya shafa akwai ƴan bijilante da kuma wani mutum guda da ƴan fashin dajin suka kashe a ranar Lahadi. Akwai kuma wasu mazauna ƙauyen da aka yi garkuwa da su a gonakinsu dake wajen Sabon Layi dukkansu a ƙarƙashin mazaɓa ta.”

Shima mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Kaduna, Mansir Hassan ya tabbatar da kisan mutanen.

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...