Ƴan Fashi Sun Kashe DPO A Jihar Katsina

A ranar Asabar, an ruwaito cewa wasu ’yan fashi sun kashe CSP Muhammad Sani Kabir, Shugaban ‘Yan Sanda na Rimi, yayin wani aikin kama masu satar shanu a Jihar Katsina, a cewar gwamnatin jihar.

Ma’aikatar Tsaro ta Cikin Gida ta jihar ta tabbatar da cewa an kashe mutane uku da ake zargin masu satar shanu ne a yayin aikin haɗin gwiwa da jami’an tsaro da mazauna unguwa suka gudanar.

A cikin wata sanarwa, Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida, Nasir Mu’azu, ya bayyana alhini kan rasuwar jami’in wanda ya yi musayar wuta da ’yan fashin kai tsaye yayin jagorantar aikin.

Sanarwar ta ce rahotanni daga shugabannin al’umma, ciki har da shugaban APC, shugaban ƙauyen Karare da shugaban Rimi, sun nuna cewa an ga masu satar shanu a garin Magaji, karamar hukumar Maje-Gobir. Bayan tabbatarwa, DPO ya jagoranci jami’an tsaro zuwa wurin.

More from this stream

Recomended