Ƴan Boko Haram sun yi garkuwa da wani alƙali da matarsa a jihar Borno

Mayaƙan ƙungiyar Boko Haram sun yi garkuwa da alƙalin babbar kotu mai Shari’a, Haruna Mshelia tare da matarsa da kuma dogarinsa.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin akan hanyar  Buratai zuwa Buni-Gari a lokacin yake kan hanyarsa ta dawowa daga birnin Maiduguri inda yake aiki.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa ƴan bindigar sun fito ne daga cikin daji inda suka rufe titin.

Wata majiya ta bayyana cewa duk da ƙoƙarin da direban ya yi na tserewa  wasunsu sun sake fitowa inda suka sha gabansu suka tsayar da su kana suka tasa ƙeyar mutanen da suke cikin motar ya zuwa cikin Dajin Sambisa.

Titin da lamarin ya faru  shi ne ɗaya tilo daya haɗa kudancin jihar Borno da kuma Maiduguri babban birnin jihar..

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Borno, ASP Nahum Daso ya tabbatar da faruwar lamarin.

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami'anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...