Ƴan Boko Haram sun kashe manoma a Borno

Mayakan Boko Haram sun kashe manoma 10 tare da yin garkuwa da wasu da dama a karamar hukumar Mafa da ke jihar Borno.

Baya ga wannan harin da aka kai da yammacin ranar Asabar a filayen dake tsakanin kauyukan Bulakunkumma da Maiwa na gundumar Baram Karowa ta karamar hukumar, ‘yan ta’addan sun kuma samu N4m daga hannun wani dan kasuwa a unguwar Zannari a matsayin kudin fansa.

Wata majiya mai tushe, Ya Kalu Bukar, wacce ta tabbatar da harin, ta bayyana adadin wadanda aka sacen a matsayin hudu, amma wata majiya mai suna Goni Mohammed ta ce an sace mutane har tara.

“Sun zo zagayawa cikin gonaki don neman abinci da tsabar kudi,” a cewar Bukar.

“Lokacin da manoman suka ce ba za su iya biyan kudaden da suka nema ba, sun kashe 10 daga cikinsu, dukkansu maza, suka tafi da hudu.”

More News

Jihar Neja Ta Yi Rajistar Mutane 289 Da Suka Kamu Da Cutar Amai Da Gudawa, 17 Sun Mutu

Wata annobar cutar amai da gudawa a Jihar Neja ta yi sanadin mutuwar mutane 17 tare da kama mutane 289 a kananan hukumomi 11...

Dakarun Najeriya sun cafke wasu ƴan’aiken ƴanbindiga a Kaduna

Sojoji sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da kaiwa 'yan bindiga sakonninsu a kasuwar ƙauyen SCC da ke ƙaramar hukumar Kachia a...

An ƙona sakatariyar ƙananan hukumomi 2 a jihar Rivers

Wasu da ake kyautata zaton ɓatagari ne sun ƙona wani sashe na sakatariyar ƙananan hukumomin Eleme da Ikwerre dake jihar Rivers. Ƙona ginin na zuwa...

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...