Ƴan bindiga sun yi garkuwa da wani fasto a Filato

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Sunday Agang wanda fasto ne a cocin Evengilical Church Winning All (ECWA) wanda har ila shi ne shugaban kwamitin amintattu na cocin a karamar hukumar Jos north ta jihar Filato.

A cewar Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi, lamarin ya faru ne a ranar Talata da misalin karfe 02:30 na rana lokacin da wasu yan bindiga kusan su 6 suka farma gidan faston dake unguwar Farin Gada a Jos.

” Jami’an yan sanda sun ce tuni aka ƙaddamar da aikin kuɓutar da shi inda ake cigaba da kokarin bin diddigin masu garkuwar tare da kuɓutar da shi lafiya, ” a cewar Makama.

Ya kara da cewa jami’an sun tabbatarwa da mazauna unguwar cewa ana cigaba da bincike don ganin an kama masu garkuwar.

Dickson Auta mai magana da yawun cocin ta ECWA ya tabbatar da ɗauke faston a cikin wata sanarwa da ya fitar.

Inda ya ce cocin ta damu matuka kan yadda ake samun karuwar kai farmaki kan fastocin cocin da mambobinta a jihohin Filato da Kwara.

More from this stream

Recomended